Super Falcons za ta buga Olympic karon farko bayan shekara 16

Tawagar kwallon kafa ta mata ta Nigeria ta samu gurbin shiga gasar Olympic, bayan da ta je ta tashi ba ci a South Africa ranar Talata.

Karon farko da Super Falcons za ta buga tamaula a Olympic tun bayan shekara 16, inda birnin Paris a France ne zai karbi bakuncin wasannin bana.

Ranar Juma’a suka buga wasan farko a Abuja, Nigetia, inda Super Falcons ta yi nasarar cin Banyana Banyana 1-0, kenan ta kai gasar Olympic da cin kwallo 1-0 gida da waje.

Kenan har yanzu Banyana Banyana ta kasa ganin ranar da za ta doke Super Falcons a South Africa a fannin kwallon kafar mata.

Cikin wasa 24 baya da suka kara an buga bakwai a South Africa, inda Super Falcons ta lashe 15 daga ciki da canjaras biyar, inda ta yi rashin nasara hudu.

A karawa bakwai baya a South Africa, Nigeria ta yi nasara biyar da canjaras biyu.

Leave a comment