Tawagar kwallon kafa ta mata ta Nigeria ta yi nasara a kan ta Africa ta Kudu da ci 1-0 ranar Juma’a a filin wasa na MKO Abiola da ke babban birnin tarayya Abuja, Nigeria.
Sun kara ne a wasan farko na neman gurbin shiga gasar tamaula ta mata a Olympic da za a yi a Faransa cikin shekarar nan.
Super Falcons ta ci kwallon a minti na 42 ta hannun kyaftin Rasheedat Aajibade.
Ranar Talata za a buga wasa na biyu a Loftus Versfeld a Pretoria, domin neman gurbin shiga wasannin Olympic da birnin Paris zai karbi bakunci.
Ranar Asabar Banyana Banyana ta koma Africa ta Kudu, yayin da Super Falcons za ta kai ziyara a daren Lahadi daga Lagos.