Super Eagles za ta kara da Zimbabwe ranar Lahadi

Tawagar kwallon kafa ta Najeriya za ta kara da ta Zimbabwe a wasa neman shiga gasar cin kofin duniya da za a yi a 2026.

Wannan shi ne wasa na bibiyu da za a buga a cikin rukuni, inda Najeriya ta tashi 1-1 da Lesotho a Uyo ranar Alhamis.

Ita kuwa Zimbabwe ta tashi 0-0 da Rwanda a wasan farko a cikin rukuni na ukun da suka yi ranar Laraba.

Zimbabwe tana buga wasanninta a Rwanda, bayan da filayaenta ba wanda yake da darajar da ake bukata.

Tuni dai Super Eagles ta samu gurbin shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka da za a buga a Ivory Coast daga Janairu zuwa Fabrairun 2024.

Super Eagles ba ta samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya da aka yi a Qatar a 2022, bayan da Ghana ta yi mata fancale.

Wasu wasannin da za a buga ranar Lahadi:

Burundi da Gabon  

Mozambique da Algeria 

Saliyo da Masar      

Sudan da Jamhuriyar Congo

Leave a comment