Real Madrid ta yi waje da Man City daga Champions League

Manchester City ta yi ban kwana da Champions League na bana, sakamakon da Real Madrid ta fitar da ita da cin 5-1 gida da waje.

Ranar Talata ƙungiyar Spaniya ta je Etihad ta ci Manchester City 2-1 a wasa na biyu a gasar da aka bai wa Bernardo Silva jan kati tun a minti na 20 da take leda.

Real Madrid ta ci ƙwallayen ta hannun Vinicius Junior ta farko a bugun fenariti, yayin da Erling Haaland ne ya ci wa City ƙwallon ta tilo.

Wannan shi ne karo na 17 da suka fuskanci juna a tsakaninsu a gasar zakarun Turai, inda Real Madrid ta yi nasara bakwai da canjaras biyar, City ta ci biyar daga ciki.

A wasan farko da suka buga a makon jiya a gasar ta zakarun Turai a Sifaniya, Real ce ta yi nasara 3-0, kenan ta kai zagayen kwata fainal da cin 5-1 gida da waje.

Real ta kai zagayen ƴan 16 ne tun farko bayan fitar da Benfica, ita kuwa City ta kai zagaye na biyu kai tsaye a Champions League.

Da wannan sakamakon watakila Real Madrid ta fuskanci Bayern Munich a zagayen ƴan takwas, bayan da ƙungiyar Jamus ta sharara 6-1 a ragar Atalanta, waɗanda za su buga wasa na biyu ranar Laraba.

Kenan watakila Bayern Munich ta ɗauki fansa a kan Real Madrid, wadda ta fitar da wadda take ta ɗaya a teburin Jamus karo bakwai a Champions League.

Yanzu dai abinda ya rage a gaban City shi ne wasan karshe a Carabao Cup da Arsenal ranar Lahadi 22 ga watan Maris a Wembley.

Haka kuma City tana ta biyu a teburin Premier League da tazarar maki tara tsakani da Arsenal, wadda ke jan ragama.

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top