Marco Rose ya ce RB Leipzig za ta yi kokarin mayar da martabarta a Manchester City ranar Talata.
City za ta karbi bakuncin kungiyar Jamus a wasa na biyar-biyar a cikin rukuni a Champions League.
Wannan shi ne karo na shida da za su kece raini a tsakaninsu, inda City ta ci uku da canajaras daya, Leipzig ta ci wasa daya.
Cikin watan Oktoba, City ta doke Leipzig 3-1 a Jamus a karawa ta bibiyu a cikin rukuni na bakwai.
City mai rike da kofin bara tana ta daya a kan teburi da maki 12, ita kuwa Leipzig mai maki tara tana ta biyu.
Dukkan kungiyoyin sun kai zagaye na biyu a gasar, illa dai ana son tantance wadda za ta yi ta farko da ta biyu a rukunin.
Daya wasan rukuni na bakwai da za a buga ranar Talata shi ne tsakanin Young Boys da Crvena Zvezda, wadanda kowacce take da maki daya.
A cikin watan Maris ne City ta doke Leipzig 7-0 a Etihad a zagayen ‘yan kungiyoyi 16 a gasar ta zakarun Turai.
A karawar ce Erling Haaland ya zura kwallo biyar a ragar kungiyar da ke buga Bundesliga.
Wasannin da za a buga ranar Talata:
- Lazio da Celtic
- Shakhtar Donetsk da Royal Antwerp
- Manchester City da RB Leipzig
- AC Milan da Borussia Dortmund
- Feyenoord da Atletico Madrid
- FC Barcelona da FC Porto
- Paris Saint-Germain da Newcastle United
- Young Boys da Crvena Zvezda