Arsenal ta kai kwata fainal a Champions League

Arsenal ta kai kwata fainal a Champions League, bayan doke Bayern Leverkusen 3-1 gida da waje.

Arsenal ta yi nasarar cin ƙungiyar Jamus 2-0 ranar Talata a Emirates a wasa na biyu a gasar ta zakarun Turai, inda Eberechi Eze da Declan Rice suka ci mata kwallayen.

A makon da ya gabata a Jamus ranar Laraba, Bayern Leverkusen da Gunners suka tashi 1-1 a wasan farko zagayen ƴan 16 a gasar ta Champions League.

Da wannan sakamakon Gunners za ta buga wasan karshe a Carabao Cup ranar Lahadi a Wembley, ita kuwa Leverkusen za ta buga Bundesliga da Heidenheim ranar Asabar.

Arsenal na fatan lashe dukkan kofin gasar bana, wadda za ta fuskanci Southampton a FA Cup a makon farko a cikin watan Afirilu.

Gunners ce ta daya a kan teburin Premier League da tazarar maki tara tsakani da Manchester City ta biyu, kuma saura wasa bakwai ya rage mata ta kare wasannin Premier na kakar nan.

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top