Kocin tawagar Germany, Julian Nagelsmann ya saka hannu kan yarjejeniyar ci gaba da jan ragamar kasar zuwa bayan gasar kofin duniya da za a yi a 2026.
Nagelsmann, mai shekara 36, ya maye gurbin Hansi Flick cikin Satumbar 2023, kuma ya ci wasa uku daga shidan da ya ja ragama kawo yanzu.
Tun farko kunshin kwantiraginsa zai kare a karshen Yuli, bayan Germany ta gama gudanar da Euro 2024.
Har yanzu ba a fara wasannin neman shiga gasar kofin duniya ba a Turai, gasar da USA da Canada da kuma Mexico za su yi hadakar karbar bakunci a 2026.
Germany ta kasa haura zagayen ‘yan 16 a manyan gasa tun daga 2016, wadda aka yi waje da ita a karawar cikin rukuni a gasar kofin duniya a Russia da kuma Qatar, wadda ta kasa yin abin kirki a Euro 2020 a England.
Germany tana rukuni daya da Scotland da Hungary da kuma Switzerland a Euro 2024.
Tun farko an alakanta Nagelsmann da cewar zai sake karbar aikin horar da Bayern Munich a karshen kakar nan, domin maye gurbin Thomas Tuchel.
Germany ta yi nasarar cin France da Netherlands a wasan sada zumunta, za kuma ta fafata da Ukraine da Greece cikin Yuni a shirin da take na taka rawar gani a Euro 2024.
An yi waje da dukkan kungiyoyin Premier League daga Champions da Europa League na bana a zagayen quarter finals Latsa nan domin ci gaba da karatu