Za a buga wasan hamayya tsakanin Pillars da Barau FC

A karshen mako ake sa ran buga wasan hamayya tsakanin Kano Pillars da Barau FC a wasan mako na 29 a gasar Premier ta Najeriya.

Dukkan ƙungiyoyin suna buga wasansu a filin da ake kira Sani Abacha da ke Kofar Mata a jihar Kano, kuma a bana Barau ce ta yi nasara a kan Pillars a karawar da aka yi ba ƴan kallo.

Barau ɗin ta ci Pillars 2-1 a cikin watan Oktoba a lokacin da ƙungiyar da ake kira sai masu gida ta koma buga wasanni a Katsina, bayan hatsaniya a karawar da ta karɓi baƙuncin 3SC.

Wannan shi ne karo na biyu da za su fuskanci juna a gasar, bayan da Barau FC ta fara buga babbar gasar tamaula ta Najeriya a bana.

Pillars mai maki 32 tana ta 17 a kasan teburi, ita kuwa Barau FC tana ta 10 da maki 37.

Shin yaya kuke ganin wasan zai kaya – ku rubuta mana ra’ayinku.

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top