Za a ci gaba da wasannin Champions League

Kawo yanzu kungiyoyi hudu ne suka ci wasa uku da suka buga a cikin rukuni a Champions League na bana.

Wadanda ake sa ran za su kai zagaye na biyu sun hada da Bayern Munich da Barcelona da Real Madrid da kuma mai rike da kofin Manchester City.

Haka kuma kungiyoyin suna daga cikin wadanda ake sa ran daya daga ciki za ta iya lashe kofin bana.

Duk wadda ta yi nasara a wasa na hur-hudu da za a buga ranar Talata da Laraba, za ta samu gurbin kai wa zagayen ‘yan 16 da za su ci gaba da wasannin.

Wasannin da za a buga Talata 7 ga watan Nuwamba

Dortmund da Newcastle

Shakhtar Donetsk da Barcelona

Atlético Madrid da Celtic

Lazio da Feyenoord

Milan da Paris St Germain

Man City da Young Boys

Crvena zvezda da Leipzig

Porto da Antwerp

Wasannin Laraba 8 ga watan Nuwamba

Napoli da Union Berlin

Real Sociedad da Benfica

Bayern da Galatasaray

Copenhagen da Man United

Arsenal da Sevilla

PSV Eindhoven da Lens

Real Madrid da Braga

Salzburg da Inter Milan

Leave a comment